Labaran Najeriya
‘Yancin El-Zakzaky Baya A Hannun El-Rufai Yake ba – IMN Sun fada wa Gwamnatin Buhari

Kungiyar Islamic Movement of Nigeria (IMN), wacce kuma aka fi sani da suna Shi’a, ta yi Allah wadai da bayanin gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari na cewa ‘yancin shugabanta, Ibrahim El-Zakzaky ya dangana ne a hannun gwamna Nasir El-Rufai na Kaduna.
Naija News ta tuno cewa yan Shi’a sun yi kiran a saki El-Zakzaky ne bayan sakin Sambo Dasuki da Omoyele Sowore.
Amma a wata sanarwa da Gwamnatin Tarayyar Najeriya a karkashin shugabancin shugaba Muhammadu Buhari ta bayar, suna mai cewa sakin jagoran Harkar Musulunci ta Najeriya (IMN) Ibrahim El-Zakzaky, ya dogara ne kawai ga gwamnatin jihar Kaduna.
Naija News Hausa ta ruwaito a baya da cewa wakilan Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), wadanda aka fi sani da Shi’a a ranar Laraba da ta gabata sun halarci hidimar coci ta Kirsimeti a wasu sassan arewacin Najeriya.
A cocin daban daban na Advent, Samaru, Zariya, jim kadan bayan kammala hidimar, shugaban kungiyar, Farfesa Isa Hassan-Mshelgaru ya ce muhinmancin halartar wannan hidimar shine inganta soyayya, hakuri da fahimta a tsakanin yan Najeriya.