Connect with us

Uncategorized

A kalla mutane 15 suka Mutu a Hatsarin Jirgin Ruwa da ya afku a Borgu, Jihar Neja

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Naija News Hausa ta karbi rahoton mutuwar Mutane goma sha biyar a wani hatsarin jirgin ruwa da ya afku a kan kogin Malale da ke karamar Hukumar Borgu ta Jihar Neja.

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (SEMA) ta bada tabbacin al’amarin ga menama labaran gidan Talabijin na Channels a ranar Laraba da ta gabata.

Bisa bayanin Darakta Janar na hukumar, Mista Ibrahim Inga, ya bayyana da cewa abin ya faru ne a karshen mako da ta wuce, amma dai da cewa hukumar ta sami sanin hakan ne a ranar Talata da yamma saboda rashin sadarwa.

Ya kara a bayanin sa da cewa rahotannin da aka tattara sun bayyana da cewa kwale-kwalen akalla na dauke ne da yawar fasinjoji 50, ya kuwa  kife da su a tsakiyar kogin.

“Ko da shike, Shugaban SEMA ya fada da cewa a yayin da aka kubutar da wasu da suka tsira, wasu da dama kuma an rasa gane ko ina ne suke, amma ana kan kokarin ceto su.”

Wadanda abin ya rutsa da su sun bayyana da cewa hatsarin ya faru ne a yayin da suke dawowa daga kasuwar Warrah, wata karamar shiya a karamar hukumar Ngaski na zuwa Sabo Yumu a karamar hukumar Borgu lokacin da hatsarin ya faru.

Duk da cewa ba a iya bayyana sakamakon hadarin ba, amma ana diba da zargin cewa wata kila lodi ne yayi wa jirgin wata.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa Koramar Malale da wasu bakin ruwa da ke a Jihar na yaduwa da kashin mutane.

Mista Inga, ya bayar da cewa Gwamnatin jihar na a shirye don magance ire-iren hatsari kamar irin wannan.

Ya kuma kara da cewa Gwamnatin Jihar na kokari da ganin cewa an karfafa da kuma samar da kayan shiga Iho ga mazauna.

KARANTA WANNAN: Katsinawa ga taku! Kalli Rawan ‘Yan Katsina da baka san da shi ba