Connect with us

Labaran Najeriya

Manyan Labarai daga Jaridun Najeriya ta ranar Litini, 21 ga Watan Oktoba, Shekara ta 2019

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wadannan ne Manyan Labarai ta Jaridun Najeriya a yau Litini, 21 ga Watan Oktoba, 2019

1. Shugaba Buhari Ya Bar Najeriya Zuwa kasar Rasha

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a yau Litini zai bar Najeriya don halartar taron kwanaki uku a Rasha da Afirka a nan Sochi, Rasha.

Naija News ta fahimta da cewa taron kolin za a fara shi ne a ranar 23 ga Oktoba zuwa 25 ga Oktoba 2019.

2. Boko Haram: Mutane Biyar sun Mutu a Munsayar wuta tsakanin ISWAP da Sojojin Najeriya a Borno

Wakilan kungiyar Islamic State West Africa County (ISWAP) sun kashe a kalla sojojin Najeriya hudu da wani mayaki a cikin jihar Borno.

A cewar majiyoyin tsaro da suka yi magana da kamfanin dillancin labarai na AFP ranar Lahadi, ya bayyana da cewa fadar ya barke ne a yammacin Asabar a yayin da sojoji suka yi wa wani ayarin ‘yan kungiyar ISWAP – wanda suka tashi daga kungiyar Boko Haram – kusa da kauyen Jakana, mai nisan kilomita 42 daga Maiduguri babban birnin jihar.

3. An samu Kama Zakin da ya Tsere a Kano

Daraktan kula da gidan namun dajin na Kano, Alhaji Usman Gwadabe ya sanar da cewa wata kungiyar kwararru sun ci nasara da kama wani zakin da ya tsere daga gidan dabbobi a jihar Kano.

Naija News ya gane da cewa mazauna yankin Kano sun kwana ne cikin fargaba bayan da aka sami labarin tseretarwar zakin daga Gidan Namun Dajin a daren jiya, kamin aka sake kama.

4. Biafra: Maman Nnamdi Kanu ta rasu

Malama Ugoeze Sally Nnenne Okwu-Kanu, mahaifiyar shugaban kungiyar ‘yan asalin Biafra (IPOB), Nnamdi Kanu ta mutu.

Kamfanin dillancin labarai na Naija News ta bayar da rahoton cewa mahaifiyar Kanu ta mutu a ranar 30 ga Agusta a Jamus, shugaban IPOB din ya ba da sanarwar a wani faifan bidiyo da Naija News ta ci karo da ita.

5. Dino Melaye ya mayarda martani ga Tsige Mataimakin Gwamnan Kogi

Sanata Dino Melaye, Sanatan da ke wakilcin APC Yammacin Kogi yayi Allah wadai da tsige mataimakin gwamnan jihar Kogi, Simon Achuba.

Naija News ta ruwaito cewa a ranar Jumma’a da ta gabata ne majalisar dokokin jihar Kogi ta tsige Achuba

6. Dalilin da Yasa Ba za a Raba Buhari da Mamman Daura Ba

Dangin Daura sun dage da cewa ba zai yiwuwa ba a raba Shugaba Muhammadu Buhari da dangin ​​sa, Mamman Daura ba.

Ka tuna da cewa matar Buhari, Aisha da kuma dangin Mamman Daura a kwanan nan sun shiga fada ga rigingimun da jama’a suka gana da shi a layin yanar gizo, anan Fadar Shugaban kasa.

7. Osinbajo Bai Amfani da Sa na Mataimakin Shugaban Kasa ba a hanyar da bai dace ba – Junaid Moh’d

Dan majalisa na jamhuriya ta biyu, Junaid Mohammed, ya ce mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo a kan matsayin sa bai yi furuci ko dauki matakin da zai sanya Najeriya a cikin rikici ba a lokacin da yake rike da mukamin Shugaban kasa.

Naija News ta ruwaito a baya da cewa Osinbajo ya maye gurbin matsayin mukaddashin shugaban kasa a lokacin Shugaba Muhammadu Buhari ya tafi kasar Ingila don hutu da kuka da lafiyar jikinsa.

Ka samu kari da Cikakken Labaran Najeriya a shafin Naija News Hausa