Connect with us

Uncategorized

El-Zakzaky: ‘Yan Shi’a na Shirin Fita Zagaye a dukan Kasa don Hidimar Shekara-Shekara

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Wakilan Harkar Musulunci a Najeriya (IMN), wadanda aka fi sani da ‘Yan Shi’a sun bayyana shirye-shiryen fara taron shekara da shekara da suka saba yi ta Arba’een a kasar, a ranar Asabar din nan.

Naija News ta bayar da rahoton cewa IMN ta ba da tabbacin cewa hidimar tasu za ta kasance cikin lumana kuma ba ta da duk wani yunƙurin wargaza tafiya da fitar mutane a kan hanya a ranar.

Ka tuna a baya  da cewa Farmaki ya tashi tsakanin Jami’an tsaro da ‘Yan Shi’a a birnin Tarayya, Abuja, bayan da IGP Mohammed Adamu, shugaban ‘yan sandan Najeriya ya bayar da umarni cewa a kama dukan shugabanan kungiyar Harkan Musulunci ta Najeriya (IMN) da aka fi sani da Shi’a.

Farmaki da ya faru a Abuja ya haifar da kashin wani babban Jami’in tsaro tare da wasu mambobin shi’a.