Kalli Jerin Kwararrun ‘Yan Fim Na Hausa Da Muke Da Tarihin Rayuwarsu A Rubuce

Naija News Hausa a sashen mu ta Nishadi mun ruwaito da Tarihi da Takaitaccen Labarin ‘yan shirin fim a Kannywood da dama cikin ‘yan watanni da suke shige.

Na farko a jerin tarihin ‘yan kannywood da Naija News Hausa ke dauke da shi itace Fati Washa, ba son kai ko wata ban girma ba amma itace na farko da kuma wacce aka fi neman karanta tarihinta a shafin mu.

Karanta Jerin suna da Adadin labaran rayuwarsu a kasa;

1. Fati Washa

Fatima Abdullahi Washa sananiyar akta ce a Kannywood. Sunar ta a filin wasa itace Fati Washa.  an haife ta ne a Watan Biyu 21, 1993, a Jihar Bauchi. a santa da sunaye kuma kamar haka; Tara Washa ko kuma Washa. A shekara ta 2018, Fati Washa na da shekaru 25. Kuma bata da Aure. Kyakyawa ce kuma da hasken jiki, Fati Washa tana daya cikin masu tsarin fim wanda ake fahariyya da su a Kannywood.

Akwai sani da cewa ita Kyakyawar yarinya ce kuma daya daga cikin yan wasan fim dake da tsadar kamu a Kannywood. Da yawa a cikin masoyan ta kan so ta a nishadi da kuma neman ta a facebook da sauran fillin nishadi don darajata ta ga aikin ta. Ci gaba da karanta labarin Fati Washa.

2. Ali Muhammad Idris (Ali Art Work)

Dan matashin mai suna Ali Muhammad Idris da aka fi sani da Ali Artwork, an haife shi ne kuma ya girma ne Jihar Kano, a Yankin Tarauni ta Jihar Kano.

Kamar yadda na san kuna muradi na so gane ko shi dan shekara nawa ne

An haife Ali Muhammad Idris ne a ranar 1 ga Watan Janairu, a shekara ta 1992.
Ya fara makarantar firamare ne a wata Makaranta mai Suna Unguwan Uku Firamare Sukul a shekara ta 1999 zuwa shekara ta 2005. ya karasa da karatun sa a Makarantar sakandare farko watau (JSS 1) a Wata Makarantar sakandare ta gwamnati daga shekara ta 2005 zuwa 2008,  bayan kammala wannan ya samu dace da ci gaba da karatun sakandaren a wata sakandare na Kundila, watau GSS Kundila daga Shekara ta 2008 zuwa 2011. Ci gaba da karanta labarin Ali Art Work.

3. Ummi Ibrahim – Zee Zee

An haifi Ummi ne a Jihar Borno a shekara ta 1989. Tsohon ta Ba’Fullace ne, uwar kuwa ‘yar Arab ce.

Ummi ta bayyana shahararun ‘yan wasa da ta ke ji d su da kuma take koyi da su sosai wajen shiri.

“Wadanda na ke ji da su kuma na ke koyi da su a filin wasan Kannywood sune kamar haka; Marigayi’a Aisha Dan-Kano da Marigayi Rabilu Musa Dan-Ibro. muna ba wa juna girma sosai da gaske, Allah ya gafarta masu” in ji ta a wata ganawa da ta yi da manema labaran (Information Nigeria) shekara da ta gabata. Ci gaba da karanta labarin Zee Zee.

4. Sani Danja

Sani Danja, kamar yadda aka fi sanin sa da suna, daya ne daga cikin shaharrarun ‘yan shirin fim ba Kannywood da ake ji da su.

Ainihin sunansa Danja ita ce; Sani Musa Abdullahi, ko kuma Sani Musa Danja.

An haifi Sani Danja ne a ranar 20 ga watan Afrilu ta shekarar 1973 a nan garin Fagge, ta Jihar Kano, a kasar Najeriya. Bincike ya bayyana da cewa Sani Musa Abdullahi ya samu likin Danja ne a lokacin da yake karami, dalilin suna kuwa itace irin halin da Sani ke da shi na rashin ji a lokacin. Kawai abokanan wasa suka laka masa sunan ‘Danja’ wanda a yau ko ina ka kira Sani Danja an riga an gane ko da wa kake. Ci gaba da karanta labarin Sani Danja

5. Rahama Sadau

An haifi Rahama Ibrahim Sadau ne a ranar 7 ga watan Disamba, a shekarar 1993 kamar yadda ‘Wikipedia’ ta bayar. Ta kuma yi zaman rayuwarta ne da iyayen a Jihar Kaduna tun daga haifuwa.

Rahama Sadau tayi karatun jami’a na farko ne a Makarantan Fasaha ta Jihar Kaduna da aka fi sani da (Kaduna Polytechnic), inda ta karanta ‘Business Administration’ a matsayin kwas na ta.

Sadau, ta kara da karatun ta na karanta kwas din ‘Human Resource Management‘ a wata babban Makarantar Jami’ar Eastern Mediterranean University in Northern Cyprus a shashin bincike akan sana’a da tattalin arziki. Ci gaba da karanta labarin Rahama Sadau.

6. Maryam Booth

Maryam Ado Muhammed, wata Kyakyawa da aka fi sani da Maryam Booth, Shahararra ce a fagen wasan kwaikwayo na Kannywood, Tana kuma da Fasaha wajen aikin Dinke-dinke.

Maryam Ado Muhammed ‘yar haifuwar Jihar Kano ce a arewacin Najeriya, an kuma haife ta ne a ranar 28 ga Watan Oktoba, a shekaran 1993.

Mahaifiyarta Maryam kuwa Ita ce, Zainab Booth, Ita ma kwararra ce kuma daya daga cikin wadanda suka dade a shirin wasan kwaikwayo na Kannywood. Haka Kazalika dan uwan Maryam, watau Ahmed Booth, shi ma Gwarzo ne a filin hadin Fim na Kannywood.

Ko da shike Kaka ta Mace ga Maryam Fulani ce, amma Kakanta namiji dan Turai ne, daga Scotland. Ci gaba da karatun labarin Maryam Booth.

7. Umar M. Sharif

Umar Muhammadu Sharif yana daya daga cikin Shahararrun mawaƙan hausa masu mahimmancin kwarari da gaske.

Sharif ba Mawaki ne kawai ba, Dan kasuwanci a fagen wasa, yana kuma da kyautannai lambar yabo mai yawa da ya karba a fagen shiri.

An haifi Sharif ne a shekarar 1987, ya kuma yi karatun Makarantar Firamare da Sakandiri ne a garin su, Rigasa ta Jihar Kaduna.

Umar ya bayyana da cewa shi ya kasance ne dalibi mai mahimmanci kuma tun lokacin yarantakarsa, abin da ya sa shi cikin raira waƙa shi ne wani abin da ya faru tsakanin shi da ƙaunarsa na farko, kamar yadda ya fada wa BBCHausa. Ci gaba da karatun labarin Umar M. Sharif.

8. Ali Jita

Ali Jita shahararran mawaki ne mai zamaninsa a Kano, sananne ne kuwa a wake-wake a fagen shirin finafinan Hausa, kuma ya shahara kwarai da gaske a yawancin finafinan hausa.

Ainihin sunan sa itace Ali Isa Jibril, kuma an haife shi ne a unguwar gyadi-gyadi a cikin badalar Kano dake a Arewacin Najeriya.

Ali yayi karatun farkon sa na Firamare ne a wata makarantar da Sakandare duk a birnin Legas, a wata makarantar sojojia, kamin dada ya bar Legas zuwa brinin Tarayyar kasa, Abuja. Ci gaba da karanta labarin Ali Jita.

9. Bilikisu Shema

Kyakkyawa da kuma shahararriyar, Bilkisu asalinta ‘yar Jihar Katsina ce. An haifi Bilikisu Shema ne a ranar 28 ga Watan Yuli a shekarar 1994.

Fitacciyar, Shema ta fara karatun ta na firamari ne a makarantar Isa Kaita College of Education, bayan nan ta shiga sekandari a Government Day Secondary School Dutsin-Ma.

Naija News Hausa ta gaza da samun tabbacin karatun babban jami’ar jarumar a wannan lokaci, idan hakan ya samu, zasu sami karin bayani.

Shema dai a cikin tashe a fagen fim a wannan lokaci, ita ce matashiyar jaruma wadda tauraronta yake haskawa. Ci gaba da karanta labarin Bilikisu Shema.

10. Jamila Nagudu

A takaice dai, Jaruma Jamila Nagudu ‘yar wasan finafinan Hausa ce wacce aka Haifeta a ranar 10 ga watan Agusta.

Jamila Umar Nagudu a nata bangaren Sarauniyar Kannywood ce, ma’ana, ita babbar jaruma mace ne a fagen shirya fina-finan Hausa, watau Kannywod wacce take da hedkwatarta a Kano, arewacin Najeriya.

Jarumar ta shiga fagen masana’antar fim na Hausa ne shekaru da yawa baya, amma ‘yan shekaru da suka gabata, babban Froduza na fina-finai, Aminu Saira ya sanyata a cikin fitaccen fim din da aka yi wa take ‘Jamila da Jamilu’, watau tun a fim dinne tauraron jaruma Jamila ya haska da bayyana ta ko ta ina saboda irin kwarewa da taka rawar gani a fim din. Ci gaba da karanta labarin Jamila Nagudu.

11. Nafisat Abdullahi

Nafisat Abdulrahman Abdullahi, wadda akafi sani da Nafisat Abdullahi, kyakyawa ce da kuma shahararrar ‘yar shirin fim a Kannywood, watau kamfanin hadin fim na Hausa a Najeriya.

An haifi Nafisat ne a ranar 23 ga watan Janairu ta shekarar 1991 a garin Jos, babban birnin jihar Filato.

Nafisat ita ce ‘ya ta hudu ga Mallam Abdulrahman Abdullahi, wani dillalin motoci da kuma dattijo masu ruwa da tsaki a kasar.
Naija News Hausa ta fahimci cewa kyakyawar tayi karatun ta na farko ne a Makarantar ‘Air Force Private School’ a nan Jos, bayan nan ta koma Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, inda ta shiga makarantar Sakandare ta Gwamnati, Dutse, Abuja. Ci gaba da karanta labarin Nafisat Abdullahi.

Ka lasa shafin Nishadi a Naija News Hausa a koyaushe don samun labaran ‘yan shirin fim na Hausa da kuma manyan labaran Nishadi ta kowace rana.

Kannywood: Hotuna da Takaitaccen Labarin Rayuwar Bilkisu Shema

A wannan karamar hirar, Naija News Hausa na gabatar maku da daya daga cikin ‘yan mata da suka yi saurin tashe wajen shirin fina-finai na Hausa a karkashin kungiyar ‘yan fim da aka fi san da Kannywood, mai suna Bilkisu Shema.

Kyakkyawa da kuma shahararriyar, Bilkisu asalinta ‘yar Jihar Katsina ce. an haifi Bilikisu Shema ne a ranar 28 ga Watan Yuli a shekarar 1994.


Fitacciyar, Shema ta fara karatun ta na firamari ne a makarantar Isa Kaita College of Education, bayan nan ta shiga sekandari a Government Day Secondary School Dutsin-Ma.

Naija News Hausa ta gaza da samun tabbacin karatun babban jami’ar jarumar a wannan lokaci, idan hakan ya samu, zasu sami karin bayani.

Shema dai a cikin tashe a fagen fim a wannan lokaci, ita ce matashiyar jaruma wadda tauraronta yake haskawa.

Sanadiyar Haskawar Tauraron Bilikisu Shema:

‘Tabbatacce Al’amari’, wannan fim shi ne wanda ya sanya wannan jaruma darewa matsayi na daya a cikin jarumai mata a kannywood domin ta tsaga a tsakiyar gogaggu ta kuwa nuna gwaninta.

Kasancewar labarin fim din kusan a kanta yake, hakan ya bata damar taka rawarta har da tsalle. Domin mafiya yawan wadanda suka kalli shirin maganar ta kawai suke yi ba ta sauran jaruman ba.

A wata Hira Bilkisu ta shaida cewa tun bayan da tayi fim din farko taso tayi aure domin har ta daina karbar aiki, amma Allah cikin ikonsa bai nufi yin auren ba, duk dai bata sanar da dalilin da ya hana yin auren ba.


Yan mata da samari na fuskantar kalu bale da yawa daga ciki da wajen masana’antar fina-finai a kokarin su na tabbatar da burin su na zama manyan taurari, amma Bilkisu tun bayan tabbataccen Al’amari Ali Nuhu ya saka ta a wani Sallamar so, sai kuma finafinai irinsu Dawood, Ranah da dai sauransu wanda yanzu haka suna hanya basu fito ba,
Ita ce Wadda aka shirya zata fito a cikin fim din Mansoor sai ta makara ba ta zo da wuri ba har aka canja ta da wata.

Kannywood: Takaitaccen Labarin Nafisat Abdullahi

Nafisat Abdulrahman Abdullahi, wadda akafi sani da Nafisat Abdullahi, kyakyawa ce da kuma shahararrar ‘yar shirin fim a Kannywood, watau kamfanin hadin fim na Hausa a Najeriya.

An haifi Nafisat ne a ranar 23 ga watan Janairu ta shekarar 1991 a garin Jos, babban birnin jihar Filato.

Nafisat ita ce ‘ya ta hudu ga Mallam Abdulrahman Abdullahi, wani dillalin motoci da kuma dattijo masu ruwa da tsaki a kasar.

Karatun Nafisat Abdullahi

Naija News Hausa ta fahimci cewa kyakyawar tayi karatun ta na farko ne a Makarantar ‘Air Force Private School’ a nan Jos, bayan nan ta koma Babban Birnin Tarayyar Najeriya, Abuja, inda ta shiga makarantar Sakandare ta Gwamnati, Dutse, Abuja.

Tun tana yarinya, ta shiga masana’antar shirya fina-finai ta Kannywood inda ta fara shirinta a karkashin FKD Production tare da Ali Nuhu, a matsayinsa na mai bada shawara na farko a gareta.

Ta Yaya da Kuma Wani Lokaci Ne Ta Fara Hadin Fim?

Nafisat Abdullahi dai ta fara aikin fim ne tun tana ‘yar shekara 19 tare da FKD Production, a matsayin kamfanin shirya fina-finanta na farko inda ta fara fitowa a cikin fim din ‘Sai Wata Rana’ a shekarar 2010, fim da aka shirya ta hannun babban kwararre da jigo a Kannywood, Ali Nuhu.

Ainihi, Nafisat ta fara aikinta na fim ne a matsayin kwararra da farkon shekarar 2010, lokacin da ta taka rawar gani na farko a jagorancin Sai Wata Rana a matsayinta na babbar jigo a fim din.

Ta samu kyautar shiri daga ‘City People Entertainment’ a shekarar 2013 don taka rawar gani, da kuma kwarewa da lambar yabo ta Kannywood a cikin 2014 don Mafi kyawun shahararriya a Kannywood.

Kyautuka Da Nafisat ta Lashe a Shirin Fim:

Shekara      Mai Bayar da Kyauta                                Sashen Kyautar                      Fim

2013,  City People Entertainment Award    – Shahararrar ‘Yar Shirin fim  –   A Fim din (Ya Daga Allah)

2014            Kyautar Farko a Kannywood   – Fitacciyar ‘Yar Shirin Fim     –   Dan Marayan Zaki

2014            AMMA Awards                       – Fitacciyar ‘Yar Shirin Fim      –   Dan Marayan Zaki

2015           Kyautar Kannywood ta Biyu    – Kyautar Musanman a Kannywood
2016           City People Entertainment      – Fitacciyar ‘Yar Shirin Fim      –     Kyautar Musanman
2016           AMMA Awards                        – Fitacciyar ‘Yar Shirin Fim      –     Da’iman
2016           Kyautar Kannywood Na Uku   – Fitacciyar ‘Yar Shirin Fim      –     Baiwar Allah

Ga Jerin Fina-Finai da Nafisat Abdullahi ta Fito a Ciki:

Ummi
Zango
Ya daga Allah
Yar Agadez
Addini ko Al’Ada
Ahlul Kitab
Alkawarina
Alhaki Kwikwiyo
Alhini
Allo (film)
Auren Tagwaye
Baban Sadik
Badi Ba Rai
Ban Kasheta Ba
Blood and Henna
Cikin Waye?
Dan Almajiri
Dan Marayan Zaki
Dare
Dawo Dawo
Farar Saka
Fataken Dare
Gabar Cikin Gida
Haaja
Har Abada
Jari Hujja
Laifin Dadi
Lamiraj
Madubin Dubawa
Guguwar So
Baiwar Allah

Takaitaccen Bayanin Rayuwar Ali Jita

Wannan Itace Taikatacen Labarin Shahararran Mawaki, Ali Jita

Ali Jita shahararran mawaki ne mai zamaninsa a Kano, sananne ne kuwa a wake-wake a fagen shirin finafinan Hausa, kuma ya shahara kwarai da gaske a yawancin finafinan hausa.

Ainihin sunan sa itace Ali Isa Jibril, kuma an haife shi ne a unguwar gyadi-gyadi a cikin badalar Kano dake a Arewacin Najeriya.

Makarantar da Ali Jita Ya Je:

Ali yayi karatun farkon sa na Firamare ne a wata makarantar da Sakandare duk a birnin Legas, a wata makarantar sojojia, kamin dada ya bar Legas zuwa brinin Tarayyar kasa, Abuja.

Mawakin ya koma jihar Kano ne bayan karatun Sakandare inda ya kammala karatun sa na Difloma akan harkar mulki da kuma a fannin na’ura mai kwakwalwa, hade da wani difloma a shafin Computer, a wata makarantar Intersystem ICT School, duk anan Kano.

Ali jita da Matarsa
Lokacin da Ali Jita Ya Fara Wake-Wake:

Shahararren, Ali Jita bisa bincike ya tsunduma a harkar wake-waken Hausa ne a tun daga shekarar 2009 a inda kuma nan da nan ya samu karbuwa a zukatan masoya da al’umma sakamakon kwarewar sa da kuma zazzakar muryar da Allah ya bashi.

Mawakin sanadiyar kwarewarshi a yanzu haka ya samu nasarori da dama inda ya lashe kyaututtuka masu tarin yawa sannan kuma ya fitar da kundin wakoki da yawa.

Wakokin Ali Jita:

Mamana, Arewa Angel, Gimbiyar Mata, Arewa, Kyece, Yara Yara, Masoyiyata Indo, Indo, Nanaye, Allah Sarkin Duniya, Farar Diya, Tarkon, Qauna, Ladidiya, Giyar Mulki, Sona Sinadari, Halimatu Sadiya, Love, Duniya, Rayuwa, Buri Uku, Fadakarwa, Mata, Watan Azumi, Zamana Aure, Rabbana, Zakka, Jawabi, Muyi Shilo da dai sauransu…

Ga sabuwar Waka Da Ali Jita ya fitar; Arewa Angel

Iyalin Ali (Watau Mata Da Yara):

Bisa bincke, Naija News Hausa ta fahimci cewa Ali Jita nada mata daya ne kawai, Allah kuma ya albarkace su da samun ‘ya’ya biyu.

Ali dai masoyin wasan kwallon kafa ne, kuma shi babban masoyin kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ne.

Ali Jita ya yi fita a shirin Fina-finai kamar su Gimbiya Bakandamiya, Kishi, Murmushin Alkawari Zaman Aure, da kuma Garin Gimba.

Kannywood: Kotu ta yanke hukunci kan Rigimar Hadiza Gabon da Amina Amal

Naija News ta ruwaito a baya da cewa Shahararriyar ‘yar shirin fim na Hausa, Amina Amal ta wallafa kara ga Kotun Koli ta Jihar Kano, a kan fadan ta da Hadiza Aliyu Gabon.

Kalli sanarwan Karar kasa;

Naija News Hausa ta kuma kula da cewa kamfanin ‘yan shirin fim na Hausa a Kano, wanda aka fi sani da Kannywood ya kusa da rabuwa sakamakon rikice-rikice da ya afku tsakanin manya a kungiyar, kamar su Ali Nuhu, Adam A. Zango, Naburaska, Hadiza Gabon da dai sauransu.

Sabuwar rahoto da ke isa ga wannan kamfanin dilancin labarai ta mu, Naija News Hausa, na bayyana da cewa kotu ta yanke hukunci kan rikici da ke tsakanin Hadiza Gabon da Amina Amal.

Tabbacin rahoton ya fito ne daga majiyar Youtube ta Kannywood, watau ‘Kannywood Emp’.

Ga rahoton a kasa cikin Faifain bidiyon da aka rabas;

Sarki Mai Sangaya: Jarumi, Ali Nuhu ya ce ba shi da budurwa a Kannywood

Babban Jarumi da Kwararre a shafin hadin fim na Hausa da aka fi sani da Kannywood, Ali Nuhu ya bayyana da cewa mata guda daya kacal yake da burin mallaka a rayuwarsa.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa jarumin ya fadi hakan ne a wata hira da ya yi da kamfanin dilancin labarai ta BBC Hausa, a inda jarumin ya jaddada da cewa a bayan Maimuna matarsa, bashi da muradin kari domin ita daya ta ishe shi zaman gidan duniya.

A cikin hirar mai tsawon ‘yan mintoci hudu, jarumin da aka tambayeshi yawan yaran da yake burin ya haifa a rayuwarsa, sai ya amsa da cewa lallai yara hudu kacal yake son ya haifa, amma kuma Allah ne ya baiwa kansa sani.

Hira tayi dadi sai ga tambaya mai zafi, Am tambayi Ali iya yawan ‘yan mata da yake da shi a Kannywood, jarumin kuwa da murmushi ya amsa da bayyana cewa bashi da ‘yan mata sai dai ‘ya’ya. Ya kuwa bayyana sunayen yaran nasa a matsayin Hadiza Gabon, Maryam Yahaya da dai sauran su.

Shin wani irin shawara ne aka fi baka? Jarumin ya bayyana a fili da cewa lallai an fi bashi shawara ne kan abubuwan da suka shafi harkokin sana’arsa, da kuma dangantakarsa da mutane. A karin bayani, jarumin ya bayyana Hafiz Bello a matsayin na hannun damarsa a masana’antar duk da cewar ba kasafai ake ganinsu tare ba.

Ya kara da cewa zamaninsu ya taso ne tun yarantaka. Ya kuma bayyana cewa darakta Hafiz shine mutumin daya da basu taba samun tangarda da shi ba a Kannywood.

Kali Bidiyon Hirar Jarumi Ali Nuhu da BBC Hausa a kasa;

 

Sabuwar Waka: Sirrin Soyayya – daga bakin Ahmed Musa Oxford da Rukky Ilham

Kalla ka sha dadin nishadin sabuwar wakar hausa da Ahmad Musa Oxford hade da Rukky Ilham suka fitar ba da jimawa ba.

Naija News Hausa ta gano wannan ne a layin yanar gizon nishadarwa ta Kannywood, watau shafin nishadi ta kungiyar shahararrun masu shirin fim na hausa.

Kalli bidiyon wakar a kasa;

Kannywood: Kalli Hotunan Fati Washa da Masoya Suka yi Allah Wadai da shi

Sharararriyar da jaruma a shafin shirin fim a Kannywood, Fati Washa a ranar bikin samun ‘yancin kai na Najeriya da aka yi ranar Talata 1 ga watan Oktoba 2019 da ta gabata, ta fitar da wasu hotuna da masoyanta suka yi Allah wadai da ita.
Naija News Hausa ta tuna da cewa a ranar, al’ummar kasar hade da jarumai da yawa sun fito don nuna farin cikinsu da zagayowar cika ga karin shekara a samun yancin kai ga kasar Najeriya. A yayin murnan ne aka hango wasu hotuna da jaruma Fati Washa ta rabar a layin yanar gizon nishadarwa. Hotunan da a halin yanzu ya yadu a shafukan sada zumunta ya nuna inda Fati tayi ado sanye da kaya masu launin kore da fari, ma’ana masu kama da tutar Najeriya.
Sai dai, hotunan jarumar ya jawo kace nace a tsakanin al’umma inda mutane da yawa suka dinga to fa albarkacin bakinsu akan yanayin shiri da fitan jarumar a cikin hoton da ta rabar da kanta. Naija News Hausa ta kula bisa bayanin al’umma da cewa Hotunan dai kuru-kuru sun fito da surar jikinta, wannan kuma ya sa mutane da yawa daga cikin mabiyanta suka bayyana cewa jarumar ba ta sanya rigar nono ba, ma’ana ta dauki hoton ba tare da rigar nono ba, sannan kuma gashin kanta ya fito kowa yana kallo.
Kalli Hotunan a kasa;

Sabuwar Labari: Shahararren Jigo, Adam A. Zango ya fita daga Kannywood

Shahararren Dan Shirin Fim da Jigo a Kannywood, Adam A. Zango ya fita daga hadaddiyar kungiyar ‘yan shirin wasan fina-finai na Hausa, da aka fi sani da Kannywood.

Naija News Hausa ta sami tabbacin wannan ne bisa sanarwan da aka bayar a layin yanar gizon nishadewa ta Twitter na @KannywoodEmp.

Adam a cikin sanarwan sa da ya bayar, ya baiyana da cewa ya bar kungiyar ne saboda irin shugabanci da ake yi a kungiyar.
Sakon na kamar haka;
“Shugabanci kama karya da ake yi mai karfi, mai daukaka, mai arziki ba’a iya hukuntashi saboda kwadayi da son zuciya” inji Adam.

Naija News Hausa ta fahimta da cewa wannan ya biyo bayan wata hadarin mota da Adam A. Zango yayi da motar sa, ko da shike abin ba zan da yawa ba amma bisa sanarwa da aka bayar a Kannywood, hadarin ya faru da shi ne a yayin da yake kan dawo wa daga kasar Nijar.

Ga sanarwan a kasa;