Connect with us

Uncategorized

Shiites: Kalli Hotunar Isar El-Zakzaky da Matarsa a kasar India a yau

Published

on

at

Listen to article
0:00 / 0:00

Bayan hukunci da Kotun Koli ta Jihar Kaduna ta bayar ga sakin Sheikh Ibrahim El-Zakzaky, shugaban Kungiyar ci gaban Harkar Musulunci (IMN) da aka fi sani da ‘Shi’a, rahotannai sun bayyana da tashin El-Zakzaky da Matarsa zuwa Turai daga birnin Abuja a jiya, Litini, 12 ga watan Agusta.

A yau Talata, 13 ga watan Agusta 2019, Naija News Hausa ta karbi rahoto da tabbacin isar El-Zakzaky da Matarsa Zeenat, a kasar Indiya.

Ka tuna da cewa ‘Yan Kungiyar shi’a a baya sun tayar da zanga-zanga a kasar da bukatar a saki shugaban su. Har ma sanadiyar hakan, an kashe rayuka da dama a birnin Tarayya, da kuma barin mutane da yawa da raunuka.

Hotunan da ke kasa da Naija News ta ci karo da shi ya bayyana tabbacin isar El-Zakzaky da matarsa a kasar Indiya don binciken Lafiyar Jikunansu.

Kalli Hotuna;